Lamarin dai ya auku ne a lokacin da bakin mahalarta bikin auren gargajiyar suke kokarin komawa gidajensu bayan kammala shagalin bikin, inda kwale-kwalen da suke ciki ya kife a kogin Niger, dake yankin Lafiagi a yammacin jihar Kwara.
Jami'an 'yan sanda da sauran majiyoyi sun sanar da cewa, fasinjoji 21 ne a cikin kwale-kwalen a lokacin da ya kife. Kuma mutane biyu ne kadai suka tsira a hadarin.
Masu aikin ceto sun riga sun tsamo gawarwakin mutanen 19.
Ajayi Okasanmi, kakakin hukumar 'yan sandan jihar Kwara, ya shedawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, hukumar 'yan sanda da sauran hukumomin tsaro a yankin sun fara gudanar da bincike domin gano musabbabin da ya haddasa faruwar hadarin. (Ahmad Fagam)