Jami'in asusun IMF ya ce zurfafa manufar bude kofa ta kasar Sin zai inganta samar da ci gaban kasar
Babban masanin tattalin arziki na asusun bada lamuni na duniya IMF wato Maurice Obstfeld, ya ce zurfafa manufar kasar Sin ta bude kofa ga zuba jari da cinikayya ga kasashen duniya, zai kara fadada ci gaban tattalin arziki da kwanciyar hankali, a daidai lokacin da kasar ke shiga wani babi na samun ci gaba mai inganci.
Yayin da yake ganawa da manema labaru gabanin murabus dinsa a karshen shekara, Maurice Obstfeld, ya ce manufar bude kofa da gyare-gyare da kasar Sin ta fara aiwatarwa a karshen shekarun 1970, ta yi gagarumin tasiri kan yanayin zaman rayuwa a kasar. (Fa'iza Mustapha)