in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabar IMF:Ya kamata kasashen duniya su bunkasa sabuwar alaka a tsakaninsu
2018-12-05 19:17:30 cri
Shugabar asusun ba da lamuni na duniya IMF Christine Lagarde ta yi kira ga kasashen duniya da su bunkasa sabuwar alaka a tsakaninsu.

Madam Lagarde ta yi wannan kira ne a jiya Talata, yayin da take jawabi a dakin karatu na majalisar dokokin Amurka dake birnin Washington D.C. Jawabin uwargida Lagarde shi ne na baya-bayan a jerin laccocin Kissinger da ake gabatarwa sau biyu a shekara, inda ake gabatar da manufofin ketare da alakar kasashen duniya.

Shugabar ta kuma shawarci kasashe masu karfin tattalin arziki da su karfafa hadin kai a manyan fannoni hudu da suka hada cinikayya da harajin kasa da kasa da sauyin yanayi da yaki da cin hanci da rashawa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China