in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hadin gwiwar Sin da Afrika ya ba nahiyar kwarin gwiwa da ilimin samun ci gaban fasaha
2018-09-03 14:22:54 cri
Daraktan sashen kula da harkokin Afrika na bankin bada lamuni na duniya Abebe Selassie, ya ce hadin gwiwar Sin da Afrika a fannoni mabanbanta, ya ba nahiyar gwarin gwiwa da ilimin samun ci gaban fasaha da dorewar tattalin arziki.

Abebe Selassie, ya ce hadin gwiwar Sin da Afrika, bai tsaya a fannin harkar kudi ba, domin hadin gwiwa ce da ta kunshi fannoni da dama.

Yayin wata hira da ya yi da kamfanin dillancin labarai na Xinhua a baya-bayan nan, ya ce a ganinsa, kasar Sin muhimmiyar kwarin gwiwa ce ga kasashe masu tasowa da kuma kasashen Afrika, wadda ta ke nuna cewa za kasa za ta iya samun ci gaba cikin sauri cikin wani lokaci, tare da tashi daga kasa mai talauci zuwa mai samun matsakaicin kudin shiga.

Ya kara da cewa, kasar Sin muhimmiyar abokiyar hulda ce a fannin cinikayya da ci gaba ga nahiyar, kuma akwai ilimi mai tarin yawa da nahiyar ta samu daga kasar Sin, ya na mai cewa bai dace a kalli hadin gwiwar bangarorin biyu ta fuska guda ba.

Ya ce taron FOCAC da za a yi yau da gobe, na zuwa ne a wani muhimmin lokaci da ake sa ran kasar Sin za ta tabbatar da kudurinta da goyon baya ga ci gaban nahiyar Afrika. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China