in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata a sabunta ra'ayoyi game da hadin gwiwar Sin da Afirka, in ji jami'in IMF
2018-10-10 10:42:06 cri
Kwanan baya, shugaban sashen Afirka na Asusun ba da lamuni na IMF Abebe Aemro Selassie, ya bayyana cewa, ya kamata a kawar da ra'ayoyin yammacin kasashen duniya, a kuma sabunta ra'ayoyin asusun a fannin hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka.

Kwanan baya, wasu kafofin yada labarai na yammacin kasashen duniya sun yi zargin cewa, ayyukan gina ababen more rayuwa da kasar Sin ta yi a kasashen Afirka, za su kawo wa kasashen Afirka babbar matsala ta bashi. Dangane da wannan lamari, Mr. Selassie ya ce, a halin yanzu, kasashen Afirka guda 6 zuwa 7 ne kadai suke fama da matsalar bashi, ko kuma suke fuskantar babban kalubale na shiga cikin wannan matsala, kuma sun samu rancen kudadensu ne daga kasashe daban daban, ba wai kasar Sin ita kadai ba.

Ya kara da cewa, jarin da kasar Sin ta zubawa kasashen Afirka, ba kawai domin su biya bukatun kasashen Afirka ba ne, har ma ana fatan za su samar wa kasashen babbar moriya. Ana da imanin cewa, kasashen Afirka za su iya neman dauwamammen ci gaba, da kuma rage kalubalen bashinsu, bisa jarin da kasar Sin ta samar musu, da kuma karin hajojin da za su fitar zuwa kasar ta Sin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China