in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An harbe 'yan ta'adda 450 a kasar Masar
2018-10-17 10:38:01 cri
Rundunar sojan kasar Masar, ta bayyana a jiya cewa, karkashin "matakin Sinai na shekarar 2018" da aka kaddamar domin yakar ta'addanci a watan Faburairun bana, an harbe 'yan ta'adda 450, a yankunan dake arewa da kuma tsakiyar tsibirin Sinai, kana 'yan sandan da suka rasa rayukansu a cikin ayyukan yakar ta'addanci sun kai 30.

Kakakin hukumar sojan kasar Masar Tamer El-Refai, ya fadi haka ne a jiya, lokacin da yake ganawa da manema labaru, inda ya ce an gudanar da dukkan ayyukan yakar ta'addanci ne a wuraren da suke waje da unguwannin jama'a, sun kuma samu goyon baya daga wajen mazauna wurin.

A shekaranjiya Litinin ne, shugaba Abdel Fattah al Sisi na Masar, ya sa hannu kan umurnin kara watanni 3 kan wa'adin dokar ta baci da aka kafa a fadin kasar a watan Aflilun shekarar 2017.

An kaddamar da "matakin Sinai na shekarar 2018" ne a ranar 9 ga watan Faburairun bana, domin dakile kungiyoyin ta'addanci da 'yan ta'adda, wadanda ke zaune a tsibirin Sinai. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China