in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wata kotu a Masar ta ayyana wasu masu tsattsauran ra'ayin Islama 164 a matsayin jagororin 'yan ta'adda
2018-10-29 10:55:17 cri
Kamfanin dillancin labaran MENA ya ruwaito labarin cewa, a jiya Lahadi, wata kotun dake kasar Masar ta ayyana wasu masu tsattsauran ra'ayin Islama su 164 a matsayin shugabannin kungiyoyin 'yan ta'adda, ciki har da jagororin 'yan ta'addan kungiyar al-Jamaa al-Islamiya, gami da masu biyayya ga manufofin kungiyar Muslim Brotherhood wato kungiyar 'yan uwa musulmi.

Kotun hukunta manyan laifuffuka ta Alkahira ta kuma bada umurnin kwace dukiyoyin wadannan mutane, don kwamiti na musamman ya kula da su.

Akasarin masu tsattsauran ra'ayin Islama da masu biyayya ga manufofin kungiyar 'yan uwa musulmi ne ake tsare da su a gidan kurkuku, ko kuma gudun-hijira suke a halin yanzu, bayan da aka hambarar da tsohon shugaban kasar Masar Mohamed Morsi a farkon watan Yulin shekara ta 2013.

An yankewa Morsi hukuncin daurin shekaru 20 a gidan kaso sakamakon hura mummunar wutar rikicin da ake tuhumarsa a tsakanin magoya bayansa da masu adawa da shi a karshen shekara ta 2012. Haka kuma an yanke masa hukuncin daurin shekaru 25 saboda ya bayar da wasu bayanan sirri ga kasar Qatar.

Bayan da aka kifar da gwamnatin Mohamed Morsi, kasar Masar ta sha fuskantar jerin hare-haren ta'addanci da dama, al'amuran da suka hallaka daruruwan 'yan sanda da sojoji gami da fararen-hula a kasar. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China