in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Sudan da Masar sun amince su tura sojoji kan iyakokinsu
2018-11-26 09:04:51 cri
Babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Sudan Kamal Abdulo-Marouf ya bayyana cewa kasarsa da kasar Masar sun amince su tura sojoji da za su rika yin sintiri a kan iyakokinsu baya ga wata rundunar yaki da ayyukan ta'addanci da kasashen ke fatan kafawa a nan gaba.

Kasashen biyu sun cimma wannan matsaya ce a jiya Lahadi bayan wata ganawa da ministan tsaron kasar Sudan Awad Ibn Aouf ya yi da takwaransa na kasar Masar Mohamed Zaki a Khartoum, babban birnin kasar Sudan.

Kamal Abdul Marouf ya ce tattaunawar sassan biyu ta yi armashi, kasashen biyu sun kuma amince su kafa ayyukan hadin gwiwa ta hanyar musayar kwasa-kwasan horas da jami'an sojojin kasashensu.

Jami'in ya kara da cewa, kasashen Sudan da Masar sun kuma amince su karfafa alakarsu a dukkan fannoni, da karfafa alaka bisa manyan tsare-tsare da kulla alakar aikin soja bisa manyan tsare-tsare daga dukkan fannoni.

A ranar Asabar din da ta gabata ce dai ministan tsaron kasar ta Masar ya isa Khartoum don gudanar da ziyayar aiki ta kwanaki biyu a kasar Sudan. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China