Bangarorin dake tattaunawa kan yankin arewacin Afrika na Yammacin Sahara da ake takaddama a kai, sun kammala taron yini biyu a jiya Alhamis, inda manzon musammam na Sakatare Janar na MDD Horst Kohler ya ce sun amince a ci gaba da tattaunawar.
Horst Kohler ya bayyanawa manema labarai a ofishin MDD dake Geneva cewa, sun kammala tattaunawa mai zurfi, sannan ya jinjinawa wakilan bangarorin bisa tattaunawar da aka yi a bayyane kuma cikin mutunci. (Fa'iza Mustapha)