in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bankin duniya: Tattalin arzikin kasashen Afirka dake kudu da Sahara zai karu da kaso 3.2 a shekarar 2018
2018-01-10 20:37:48 cri
Wani sabon rahoto da bankin duniya ya fitar ya nuna cewa, tattalin arzikin kasashen Afirka dake kudu da hamadar Sahara zai karu da kaso 3.2 cikin 100 a shekarar 2018 da kuma kaso 3.5 cikin 100 a shekarar 2019.

A cewar sabon rahoton wanda ke bayani game da makomar tattalin arzikin duniya wanda bankin ya fitar, an yi kiyasin cewa, a shekarar 2017 da ta gabata ci gaban tattalin arzikin shiyyar ya farfado zuwa kaso 2.4 cikin 100, bayan dan koma bayan da ya fuskanta na kaso 1.3 cikin 100 a shekarar 2016.

Wannan karuwa ta nuna yadda tattalin arzikin kasashen Angola da Najeriya da Afirka ta kudu suka farfado.

Koda yake ci gaban bai kai yadda ake hasashe ba, yayin da har yanzu shiyyar ke fama da rashin masu zuba jari da koma baya ta fannin kayayyakin da ake samarwa a cikin gida.

Sai dai rahoton ya yi hasashen cewa, tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa da kaso 2.5 cikin 100 a wannan shekara. Wannan ya biyo bayan hasashen da ake kan karuwar man da ake hakowa a kasar da yadda gyare-gyaren da mahukuntan kasar ke aiwatarwa zai farfado da bangaren da ba na mai ban a kasar.

Bugu da kari, a cewar rahoton, ana saran kasashen da ba su da albarkatu za su karu cikin sauri, a hannu guda kuma sakamakon karuwar zuba jari, an yi hasashen cewa, tattalin arzikin kasar Cote d'Ivoire zai bunkasa da kaso 7.2 cikin 100 a shekarar 2018, Senegal za ta samu karuwar kaso 6.9 cikin 100, Habasha kaso 8.2, Tanzaniya kaso 6.8, sai Kenya wadda tattalin arzikinta zai karu da kaso 5.5 cikin 100 yayin da aka samu raguwar hauhawar farashin kaya.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China