in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fi fuskantar matsalar rasa ayyukan yi a yankin Afirka da ke kudu da hamadar Sahara
2017-02-16 11:15:39 cri
A kwanakin baya ne Jaridar Daily Monitor ta kasar Uganda ta wallafa wani rahoto da ke nuna cewa, yanzu ana fuskantar matsalar rasa ayyukan yi mai tsanani a yankin Afirka da ke kudu da hamadar Sahara, kuma wannan matsala tana iya kawo illa ga burin wadannan kasashe ta fannin matsakaicin samun kudin shiga.

Rahoton ya yi nuni da cewa, koda yake ana samun ingantuwar tattalin arziki a yankin Afirka da ke kudu da hamadar Sahara ta hanyar gina muhimman kayayyakin more rayuwa, duk da haka matsalar rashin ayyukan tana kara tsananta a kasashen dake yankin. Kididdigar kungiyar kwadago ta duniya wato ILO ta nuna cewa, yawan mutanen da suka rasa ayyukan yi a yankin Afirka da ke kudu da hamadar Sahara a shekarar 2017 zai kai kashi 7.2 cikin dari bisa na bara, amma ana hasashen cewa yawansu zai karu zuwa miliyan 29. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China