in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin: ya kamata kasa da kasa su kalubalanci kasashe masu ci gaba game da cika alkawuran su na samar da gudummawa
2018-12-05 16:16:54 cri
Zaunannen wakilin Sin dake MDD Ma Zhaoxu ya bayyana a ranar 4 ga wata cewa, ya kamata kasa da kasa su kalubalanci kasashe masu ci gaba game da bukatar cika alkawuran samar da gudummawar samun ci gaba, don samar da kyakkyawan yanayin samun ci gaba ga kasashe masu tasowa, da suke samun matsakaicin kudin shiga.

Ma Zhaoxu ya yi jawabi a gun taron koli na kasashe masu samun matsakaicin kudin shiga wanda babban taron MDD karo na 73 ya gudanar, yana cewa kasar Sin kasa ce da ta samu matsakaicin kudin shiga, kana kasa ce mai tasowa. Ya ce kasar Sin za ta yi kokari tare da kasashe masu tasowa, duk da yanayin sauyi da ake samu a duniya. Kaza lika Sin na tsayawa tsayin daka kan tabbatar da moriyar bai daya ta kasashe masu tasowa, da ci gaba da yin hadin gwiwa da samun bunkasuwa tare. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China