A gun bikin bude taron a wannan rana, babban sakataren MDD António Guterres ya yi nuni da cewa, bisa rahoton bambancin fitar da abubuwa masu gurbata yanayi na shekarar 2018, wanda hukumar kiyaye muhalli ta MDD ta gabatar da ranar 27 ga watan da ya gabata, a halin yanzu alkawarin da kasa da kasa sun yi wajen rage fitar da abubuwa masu gurbata yanayi bai kai burin da aka tsara na nan da shekarar 2030 bisa yarjejeniyar Paris ba. A ganin Guterres, ana bukatar kasa da kasa su sake yin bincike kan alkawarinsu a cikin yarjejeniyar Paris don cimma burin shekarar 2030.
Tawagar wakilan kasar Sin mai halartar taron ta gudanar da taron manema labaru a wannan rana, inda ta yi bayani game da ka'idoji da matsayin kasar Sin a gun taron. Mataimakin shugaban sashen kula da yanayi na ma'aikatar harkokin yanayi na kasar Sin Lu Xinming ya yi bayanin cewa, Sin tana kula da shawarwari kan ka'idojin aiwatar da yarjejeiyar Paris a fannoni uku, wato tabbatar da gama yin shawarwarin cikin lokaci, da fahimta, da aiwatar da yarjejeniyar Paris yadda ya kamata, da kuma gudanar da yarjejeniyar a dukkan fannoni cikin adalci, da kuma maida hankali ga muhimman fannoni. (Zainab)