in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashe daban-daban sun yabawa rawar da kasar Sin ta taka lokacin da take rike da shugabancin karba-karba na kwamitin tsaron MDD
2018-12-03 20:54:39 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya bayyana yau Litinin cewa, kasar Sin ta kammala wa'adin aikinta na shugabancin karba-karba na kwamitin tsaron Majalisar Dinkin Duniya na watan Nuwamba, kuma irin rawar da kasar ta taka ta samu yabo matuka daga kasashe daban-daban.

Geng Shuang ya nuna cewa, MDD tamkar jagora ce ga hada kan kasashe daban-daban don tafiyar da harkokin duniya. A halin yanzu, kasashen duniya na matukar bukatar MDD mai karfin gaske fiye da kowane lokaci a baya. Kasar Sin za ta ci gaba da girmama ka'idoji gami da manufofin kundin tsarin mulkin MDD, da taimakawa ga daidaita batutuwan da suka jawo hankalin duniya, ta yadda MDD za ta kara taka muhimmiyar rawa a harkokin kasa da kasa.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China