in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata kasa da kasa su daidaita matsalar rashin daidaiton samun ci gaba, in ji wakilin kasar Sin
2018-07-17 13:50:57 cri
A jiya Litinin, zaunaniyyar tawagar kasar Sin a MDD tare da hadin gwiwar sashen kula da harkokin tattalin arziki da zaman al'umma na MDD da kuma hukumar raya kasashe ta majalisar, ta gudanar da babban taro mai taken "tinkarar matsalar rashin daidaiton ci gaba da tabbatar da samun dauwamammen ci gaba", zaunannen wakilin kasar Sin a MDD, Ma Zhaoxu ya halarci taron

A jawabinsa, Mr. Ma Zhaoxu ya ce, rashin daidaiton ci gaba matsala ce da kasashen duniya ke fuskanta, don haka ya kamata su hada kansu, don tabbatar da ci gabansu.

Ma Zhaoxu ya jaddada cewa, ra'ayin neman ci gaban bangare guda da kariyar ciniki na kawo barazana ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya, wanda kuma ya jawo damuwa ga kasashen duniya da rashin amincewa a tsakaninsu.

Kullum Sin na adawa da ra'ayin neman ci gaban bangare guda da kuma kariyar ciniki, kuma a ganinta, ya kamata a daidaita sabani da matsaloli yadda ya kamata. Sin na son hada kai da sassa daban daban, don kiyaye tsarin ciniki cikin 'yanci kuma tsakanin bangarori daban daban, don kiyaye muradun kasashen duniya.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China