in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dan majalisar gudanarwar Sin ya gana da shugaban babban taron MDD
2018-07-03 19:22:22 cri
A yau ne mamba a majalisar gudanarwar kasar Sin kana ministan harkokin wajen kasar ta Sin Wang Yi ya gana da shugaban babban taron MDD karo na 72 Miroslav Lajcak a nan birnin Beijing.

Yayin ganawar Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin tana goyon bayan muhimmaiyar rawar da MDD take takawa wajen tabbatar da zaman lafiya da samar da ci gaba, tana kuma goyon bayan tsarin kasancewar bangarori daban-daban da tsarin tafiyar da harkokin kasa da kasa karkashin kulawar MDD.

A nasa bangaren Lajcak ya bayyana godiya ga kasar Sin bisa goyon bayan da take baiwa tsarin kasancewar bangarori daban-daban. Ya ce gina al'umma mai kyakkyawar makoma ga bil-Adam da shawarar Ziri daya da hanya daya da kasar Sin ta gabatar za su ba da babbar gudummawa ga kokarin samar da zaman lafiya da ci gaban duniya. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China