in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Iran ta shiga cikin jerin kasashen duniya masu karfin makamai masu linzami duk da matsin lamba: ministan tsaro
2018-12-03 10:46:27 cri
Ministan tsaron kasar Iran Amir Hatami ya sanar a jiya Lahadi cewa, kasarsa ta zama daya daga cikin kasashen duniya da suke da karfin makamai masu linzami duk da irin matsin lambar da kasar ke fuskanta daga kasashen yammacin duniya cikin shekaru 40 da suka gabata.

"Iran tana daya daga cikin manyan kasashen duniya dake sahun gaba wajen kera makamai masu linzami, da jiragen sama masu bincike, da manyan tankokin yaki da sauran motocin dake daukar makamai," in ji Hatami ya fadawa kamfanin dillancin labaran kasar IRNA.

"Iran ta samu nasarar kaiwa matsayin da take son kaiwa da kuma kokarin da take yi a bangaren samar da makamai don kare kanta da al'ummar Iraniyawa, ma'aikatar tsaron Iran ta kasance mai cin gashin kanta ta fuskar tsaro duk da irin matsin lambar da take fuskanta daga kasashen duniya masu ji da kansu a cikin shekaru 40 da suka gabata," an jiyo Hatami yana wadannan kalamai. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China