in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen Iran ya ce takunman Amurka al'ummar kasar su ka shafa kai tsaye
2018-11-07 11:13:13 cri
Ministan harkokin wajen Iran Mohammad Javad Zarif, ya ce takunkuman baya-bayan nan da Amurka ta sanyawa kasarsa, ba su yi la'akari da al'ummar kasar ba.

Ya ce sabbin takunkuman hari ne ga daukacin Iraniyawa domin sun shafi al'ummar kasar kai tsaye.

Mohammad Javad Zarif, ya kuma soki Amurkar bisa kakabawa kasarsa takunkumai ba bisa ka'ida ba, yana mai cewa za ta yi nadamar matakin mara hikima da ta dauka.

Ya jadadda cewa, kasar za ta dogara da albarkatunta, kuma za ta rayu har ma ta shawo kan lokacin wuya.

A ranar Litinin ne Amurka ta sanya wasu jerin takunkumai kan bangarorin makamashi da kudin Iran, tare da sana'ar fiton kayayyaki. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China