in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakataren harkokin wajen Birtaniya zai kai ziyara Iran game da muhimman batutuwa
2018-11-19 10:39:54 cri
Sakataren harkokin wajen Birtaniya, Jeremy Hunt, zai kai ziyara Iran a yau Litinin, domin tattauna muhimman batutuwan da suka shafi kasashen biyu.

Yayin ziyarar, Jeremy Hunt zai gana da takwaransa na Iran, Mohammad Javad Zarif da wasu manyan jami'ai.

Tun bayan janyewar Amurka daga yarjejeniyar nukiliyar Iran a watan Mayu, Jeremy Hunt ne ministan harkokin wajen yammacin duniya na farko da zai ziyarci Iran.

Makomar yarjejeniyar nukiliyar Iran da matakan kasashen Turai na kare ta, su ne za su zamo kan gaba cikin jerin ajandar ziyarar Hunt.

Zai kuma tattauna kan batutuwan da suka shafi shiyyar Iran da ma dangantakar Iran da Birtaniya. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China