in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka ta sanar da sake sanyawa Iran takunkumi a fannonin makamashi da tsarin bankuna
2018-11-03 16:37:00 cri
Gwamnatin Amurka ta sanar a jiya cewa, za ta sake sanyawa Iran takunkumi a fannonin makamashi da tsarin bankuna da sauransu. Wannan ne karo na biyu da Amurka ke sanyawa Iran takunkumi bayan ta sanar da janyewa daga yarjejeniyar nukiliyar Iran a watan Mayun bana. Nan gaba, Amurka za ta mayarwa kasar dukkan takunkuman da aka soke sakamakon yarjejeniyar.

A watan Mayun bana ne, shugaban Amurka Donald Trump, ya sanar da janyewar kasarsa daga yarjejeniyar ta nukiliyar Iran. A watan Agusta kuma, ya sake sanyawa Iran din takunkumi a fannonin hada-hadar kudi da karafa da ma'adinai da motoci da sauransu. Shugaban na Amurka ya kuma bayyana cewa, za a kara mayar da sauran takunkuman a watan nan na Nuwanba.

Da take mayar da martani cikin wata sanarwa da ta fitar a jiya, ma'aikatar harkokin wajen Iran, ta ce kasar ba ta damu da takunkuman da Amurka za ta saka mata a fannonin fitar da man fetur da tsarin bankuna ba, tana mai cewa, Amurkar ta yi hakan ne don tsorata ta, sai dai hakarta ba ta cimma ruwa ba, domin kasar na da karfin raya tattalin arzikinta da tabbatar da rayuwar jama'arta bisa kowanne irin yanayi. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China