in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Nijeriya sun kashe 'yan bindiga 14 a arewacin kasar
2018-11-20 09:54:42 cri
Hedkwatar tsaron Nijeriya, ta ce sojojin kasar sun kashe 'yan bindiga 14 a jihar Kaduna dake arewacin kasar, inda cikin watanni da suka gabata aka samu jerin laifukan sace-sacen mutane.

Hukumomin tsaron sun shaidawa manema labarai jiya a birnin Kaduna cewa, an kashe 'yan bindigar ne cikin wasu jerin ayyukan soji da aka fara tun watan Oktoba.

Kakakin ma'aikatar tsaron John Agim, ya ce an kuma kwato bindigogin zamani da alburusai da garken shanu daga bata garin da suka hada da masu sace mutane don neman kudin fansa da masu satar shanu.

John Agim ya kara da cewa, baya ga haka, an ceto mutane 31 da suka hada da yara 18 da manya 13 daga wadanda suka sace su a hanyar Kaduna zuwa Abuja.

Haka zalika, ya ce an tsare tsageru 5 da masu kai musu rahoto 2, inda a yanzu suke taimakwa hukumomin tsaro a aikin bincike dake wakana. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China