in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi tir da harin da aka kai yankin tsakiyar Libya
2018-10-30 14:02:30 cri
Shirin wanzar da zaman lafiya na MDD dake Libya UNSMIL, ya yi tir da harin ta'addanci da aka kai yankin Fug'ha na lardin Jufra, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 5.

Wata sanarwa da shirin ya fitar, ta kakkausar suka kan harin na Fug'ha da hukumomi a yankin suka ce aikin ramuwar gayya ne na kungiyar IS.

Harin ya yi sanadin mutuwar fararen hula 4, inda aka kashe biyu daga cikinsu a bainar jama'a, sannan aka sace a kalla wasu 9.

MDD ta yi kira da a kare fararen hula, sannan dukkan bangarorin dake rikici su tsagaita kai hari kan fararen hula da kadarorinsu, kamar yadda dokokin jin kai na duniya suka tanada

Mutane 5 ne aka kashe da asubahin jiya Litinin a wani hari da aka kai kan wani ginin gwamnati a lardin Jufra dake yankin tsakiyar Libya, wanda ke da tazarar kilomita 650 daga birnin Tripoli. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China