in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi tir da yawaitar kashe-kashen mutane a Tripoli
2018-11-30 15:36:33 cri

Shirin wanzar da zaman lafiya na MDD dake aiki a Libya UNSMIL, ya yi tir da kashe-kashen mutane dake karuwa cikin makonnin da suka gabata a Tripoli, babban birnin Libya.

Cikin wata sanarwa da ya fitar, shirin ya ce yana ci gaba da karbar rahotannin 'yan bindiga dake aiwatar da kisa a Tripoli, yana mai jadadda cewa ya kamata a rika shigar da kararraki da sabanin tsakanin mutane gaban kotu, maimakon daukar doka a hannu.

Shirin ya kuma yi kira ga hukumomi a kasar, su gaggauta daukar ingantattun matakan kare mutane daga irin wannan kisa, tare da aikewa da sako cikin babbar murya cewa, ba za a lamunci ayyukan ba, sannan a nuna da gaske ake, ta hanyar gudanar da cikakken bincike don ganowa da hukunta wadanda ke aikata laifin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China