in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 10 sun jikkata a fashewa da ta auku a Benghazi
2018-11-22 15:19:03 cri
Jami'in watsa labarai na asibitin Al-Jalaa dake birnin Benghazin kasar Libya Fadia Al-Barghathi, ya tabbatar da jikkatar mutane 10, sakamakon wata fashewa da ta auku a birnin a daren ranar Laraba.

Fadia Al-Barghathi, ya ce biyu daga cikin mutanen da suka jikkata na cikin yanayi mai tsanani, to sai dai kuma har yanzu mahukuntan birnin ba su fitar da sanarwa game da fashewar a hukunce ba.

Birnin Benghazi, wanda shi ne birnin na biyu mafi girma a kasar Libya, ya sha fama da makamantan wannan fashe fashe a yankunan fararen hula, ciki hadda masallatai da kasuwanni. Kaza lika masu kaddamar da harin kunar bakin wake na kaddamar da hare hare, a tashoshin binciken ababen hawa dake sassan birnin. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China