in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sama da bakin haure 1330 aka tusa keyarsu daga kasar Libya a watan Oktoba
2018-10-29 09:25:37 cri
Hukumar kula da bakin haure ta kasa da kasa (IOM) ta sanar a jiya Lahadi cewa, sama da bakin haure 1330 ne aka kwashe su daga kasar Libya kana aka mayar da su kasashensu na asali a watan Oktoba.

IOM wanda ta gudanar da aikin sa kai karkashinn shirin mayar da bakin haure kasashensu na asali tare da hadin gwiwar hukumomin kasar Libyan, da nufin mayar da bakin hauren wadanda ke gararamba a kasar ta Libya.

Kasar Libya ta zama tamkar wata cibiyar da bakin haure ke ribibin zuwa da nufin tsallakawa kasashen Turai ta tekun Mediterranean sakamakon matsalar tabarbarewar tsaro da tashin hankalin da kasar ta arewacin Afrika ta tsunduma tun bayan kifar da gwamnatin tsohon shugaban kasar Muammar Gaddafi a shekarar 2011. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China