Kasar Philippines ce zangon karshe da shugaban zai ziyarta, a jerin kasashe 3 na yankin Asia da Fasifik da aka tsara zai ziyarta a wannan karo.
Tuni dai ya kammala ziyarar sa a Papua New Guinea, inda ya halarci taron shugabanni mambobin kungiyar hadin gwiwar raya tattalin arziki Asia da Fasifik karo 26, ya kuma ziyarci kasar Brunei. (Saminu Hassan)