in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Iran ya zargi Amurka da hannu a kisan Jamal Khashoggi
2018-10-24 20:15:26 cri
Kamfanin dillancin labaran kasar Iran IRNA, ya rawaito shugaban kasar Hassan Rouhani, na zargin Amurka da hannu a kisan dan jaridar nan dan Asalin kasar Saudiyya Jamal Khashoggi.

Shugaba Rouhani, ya kuma shawarci kasar Turkiyya da ya ci gaba da gudanar da sahihin bincike, domin gano gaskiyar abun da ya auku.

Jamal Khashoggi, yana aiki ne da jaridar Washington Post, kuma mai fashin baki ne da ya jima yana sukar yarima mai jiran gado na kasar ta Saudiyya. An kuma hallaka shi ne a ranar 2 ga watan Oktobar nan, a karamin ofishin jakadancin Saudiyya dake birnin Istanbul na Turkiyya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China