in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin wanzar da zaman lafiya na kasar Sin sun tashi zuwa kasar Sudan ta kudu
2018-11-14 10:50:31 cri
A ranar Litinin da dare ne wata tawaga mai dauke da ma'aikatan wanzar da zaman lafiya 180 daga kasar Sin ta tashi daga Zhengzhou, babban birnin lardin Henan dake tsakiyar kasar zuwa kasar Sudan ta kudu, inda za su shafe shekara guda suna aikin shimfida zaman lafiya.

Da yake karin haske kwamandan bataliyar Guo Meng ya bayyana cewa, tawagar ta kunshi rukunin farko na sojojin wanzar da zaman lafiya 700 da kasar Sin ta tura. Aikin da za su gudanar sun hada da kare fararen hula da ma'aikatan MDD da amsu gudanar da ayyukan jin kai da yin sintiri, da yin rakiya da sauran ayyukan tsaro.

Dukkan mambobin bataliyar dai sun shafe watanni uku suna samun horo, kuma sun ci jarrabawar da aka shirya musu, lamarin da ya sa suka cancanci gudanar da aikin kiyaye zaman lafiya a Sudan ta kudu. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China