in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta sanar da matakan kara gina rundunar sojojin saman da za ta dace da zamani
2018-11-12 10:29:09 cri
Mataimakin kwamandan rundunar sojojin saman kasar Sin Laftana janar Xu Anxiang, ya sanar da matakai uku da kasarsa ta tsara na kara gina rundunar sojojin saman kasar ta yadda za ta dace da zamani.

Laftana janar Xu wanda ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da aka shirya don murnar cika shekaru 69 da kafa rundunar sojojin saman kasar Sin da ya gudana a birnin Zhuhai dake lardin Guangdong, ya ce kara gina rundunar sojojin sama ta zamani, ya dace da manufar gina tsaron kasa da ma dakarun kasar.

A cewarsa, matakin farko shi ne,nan da shekara ta 2020, za a gina rundunar da za ta kunshi harkokin zirga-zirga da karfi a fannin sararin samaniya da ma karfin kai hari da tsaro, ta yadda sabbin kayayyakin aikin da aka tanadar za su taimakawa wadanda ake da su a halin yanzu. Wannan wani mataki ne na kara karfin rundunar a dukkan fannoni.

Mataki na biyu, shi ne bukatar kara dabarun rundunar da ma zamanantar da manufofinta,da yiwa tsari da jami'ai da daukacin makamanta garambawul. Ana kuma fatan kammala gina rundunar da za ta dace da zamani nan shekarar 2035.

Mataki na uku a cewar jami'in shi ne, nan da tsakiyar karni na 21, ana fatan yiwa bakin dayan rundunar sojojin saman kasar ta Sin gyaran fuska ta yadda za ta kasance babu irinta a duniya baki daya.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China