Shugaban kasar Sin ya ziyarci rundunar sojoji ta kudanci yana mai jaddada muhimmancin kara inganta kwarewar jagorancin sojin kasar
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya ziyarci rundunar sojoji ta Kudancin kasar a jiya Alhamis, inda ya bayyana aniyar gwamnatin sa, ta daukar matakan kara inganta kwarewar jagorancin rundunar domin samar da ci gaba.
Shugaba Xi, wanda kuma shi ne babban sakataren kwamitin koli na JKS, ya ba da umarnin aiwatar da manufofin JKS yadda ya kamata, wadanda suka tanaji karfafa rundunar sojojin kasar a sabon zamani da ake ciki.