in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin kasar Sin a MDD ya yi kira a hanzarta sake gina kasar Iraki
2018-11-14 10:41:59 cri
Wakilin kasar Sin a MDD Ma Zhaoxu, ya yi kira da a farfado da tattalin arziki da ma hanzarta sake gina kasar Iraki bayan nasarar da kasar ta samu na kafa sabuwar gwamnati.

Wakilin na Sin ya yi wannan kiran ne yayin zaman kwamitin sulhun MDD game da kasar ta Iraki, Yana mai cewa, ya kamata gwamnatin Iraki ta hanzarta aiwatar da shirinta na sake gina kasar, da ba da muhimmanci ga bangaren albartakun kasar, da bunkasa tattalin arziki da karfafa samar da horo ga ma'aikata da ma inganta rayuwar al'ummar kasar.

Jami'in ya kuma bukaci al'ummomin kasa da kasa da su baiwa kasar ta Iraki duk wani taimako da goyon baya da take bukata, da sassauta yanayin jin kai da kasar ke ciki, da taimakawa kasar a kokarin da take na farfado da tattalin arziki, da samar da yanayin da ya dace na sake gina kasar.

Ma ya kuma bayyana kudurin kasar Sin na goyon bayan duk wani mataki da ya dace na daidaita harkokin siyasar kasar da yaki da ta'addanci. Haka kuma, kasar Sin za ta shiga a dama da ita wajen sake gina tattalin arzikin kasar ta Iraki, za kuma ta ci gaba da taimakawa Irakin bisa karfinta. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China