in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Antonio Guterres ya yi Allah wadai da harin ta'addanci na birnin Mogadishu
2018-11-10 15:41:00 cri
Babban magatakardar MDD Antonio Guterres, ya yi Allah wadai da harin bama bamai na jiya Juma'a, wanda aka kaddamar a birnin Mogadishu fadar mulkin kasar Somalia, lamarin da ya hallaka a kalla mutane 15.

Cikin wata sanarwa da mataimakin kakakinsa Farhan Haq ya fitar, Mr. Guterres ya mika sakon ta'aziyya ga iyalan wadanda suka rasu, tare da fatan samun sauki cikin sauri ga wadanda suka jikkata. Ya ce MDD na da yakini game da ikon kasar Somaliya, na ci gaba da fafutukar kawo karshen tashe tashen hankula, da wanzar da zaman lafiya, tare da samar da ci gaba mai dorewa.

Daga nan sai ya nanata kudurin majalissar, na ci gaba da marawa al'ummar Somalia da gwamnatin su baya, bisa wannan muhimmin kuduri.

A kalla mutane 15 ne suka rasu, yayin fashewar wasu bama bamai uku a birnin na Mogadishu. An ce bam din farko ya tashi ne a wani Otel, sai kuma wasu karin bama baman biyu, da suka biyo baya a wani wuri maras nisa daga na farkon.

Tuni dai kungiyar Al-Shabaab ta ayyana daukar alhakin kaddamar da hare haren. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China