in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bukaci a magance matsalolin rashin tsaro daga tushe don cimma zaman lafiya a yankin Sahel
2018-11-13 10:21:37 cri
Mataimakiyar Sakatare Janar na MDD, Amina Mohammed, ta yi kira da a magance abubuwan dake haddasa rashin tsaro tun daga tushe, domin cimma zaman lafiya da ci gaba mai dorewa a yankin Sahel na nahiyar Afrika.

Yayin taron shekara na hukumar MDD mai fafutukar wanzar da zaman lafiya a yankin Sahel, Amina Mohammed, ta ce idan ana son cimma zaman lafiya da ci gaba mai dorewa, sannan a sauya daga bada agajin jin kai, zuwa ragewa da kawo karshen bukatun agajin jin kai, dole ne a magance matsalolin dake haifar da rikice- rikice daga tushe.

Ta kara da cewa, tushen wadannan matsaloli su ne nuna wariya da take hakkokin bil adama da rashin shugabanci na gari da rikici da tasirin sauyin yanayi a yankin.

Ta kara da cewa, dabara ta hadin gwiwa da za ta kunshi kowa da kowa, wadda gwamnatocin kasashen yankin za su samar, ita ce za ta taimakawa wajen samar da dawwaumamen zaman lafiya da ci gaba da ake tsananin bukata a yankin.

Har ila yau, Amin Mohammed, ta kara da bayyana kalubalen kudi da na yawan jama'a da yankin ke fuskanta, tana mai cewa jimilar abun da ake bukata na aiwatar da muradun ci gaba masu dorewa a yankin, ta kai dala biliyan 140 a bana, wadda za ta rika karuwa kowacce shekara har ta kai dala biliyan 157 zuwa shekarar 2022. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China