in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Najeriya sun kama wata 'yar kunar bakin wake
2018-11-14 09:48:47 cri
Rahotanni daga Najeriya na cewa, sojojin kasar sun yi nasarar kama wata karamar yarinya da ta tabbatar da cewa, mayakan Bokon Haram ne suka yi hayar ta don ta kai harin kunar bakin wake a garin Maiduguri dake yankin arewa maso gabashin kasar.

Wata sanarwa da sojojin suka walklafa a shafinsu na Twitter,sun bayyana cewa, yarinyar mai suna Shaidatu Adamu 'yar shekaru 19 da haihuwa, an kama ta ne a lokacin da take kokarin shiga garin na Maiduuguri, sanye da rigar kunar bakin wake.

Ta kuma shaidawa jami'an dake binckenta cewa, ta shafe kusan shekaru uku tana samun horo a dajin Sambisa. Tuni dai aka tura kwararru a fannin abubuwan fashewa domin su kwance jigidar bama-bamai dake jikinta. An kuma fara gudanar da bincike don gano inda yarinya ta nufi kai harin.

Tun a shekarar 2009 ne dai kungiyar ta Boko Haram ke kokarin kafa shari'ar musulunci a yankin arewa maso gabashin kasar ta Najeriya.

Kasashe hudu da rikicin na Boko Haram ya shafa sun hada da Chadi, Jamhuriyar Nijar da Najeriya, MDD na cewa, Boko Haram ta raba kusan mutane miliyan 2.4 da muhallansu a yankin tafkin Chadi. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China