in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar IGAD ta yabawa manufar moriyar juna ta kasa Sin, tana mai kira da karfafa dangantakar dake tsakaninsu
2018-11-13 10:37:39 cri
Kungiyar raya yankin gabashin Afrika IGAD, ta yabawa dangantakar moriyar juna da kasar Sin ke yi da kasashe mambobinta.

Sakataren zartaswa na kungiyar Mahboub Maalim ne ya bayyana haka, lokacin da yake ganawa ranar Lahadi, da Jakadan Kasar Sin a Djibouti Zhou Ruisheng.

Wata sanarwar da kungiyar ta fitar, ta ce Mahboub Maalim, ya yabawa dangantakar dake kara habaka tsakanin kasar Sin da kasashe mambobin IGAD, bisa moriyar juna da alakar kasa da kasa mai karfi.

Yayin ganawar, Mahboub Maalim, ya ce a shirye yake, ya kai ziyarar aiki ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin domin gabatar mata da manufofin kungiyar.

A wani bangare na ganawar, gwamnatin kasar Sin, ta hannu jakadan nata na Djibouti, ta mika tallafin kudi dala 100,000 ga kungiyar IGAD. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China