in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
IGAD ta yabawa nadin Raila Odinga a matsayin wakilin AU na musammam
2018-10-22 09:53:05 cri
Kungiyar raya yankin gabashin Afrika IGAD, ta yi maraba da nadin jagoran 'yan adawa na kasar Kenya, wato Raila Odinga, a matsayin babban wakilin Tarayyar Afrika ga shirin raya kayayyakin more rayuwa a nahiyar.

Sakataren zartaswa na kungiyar IGAD Mahboub Maalim, wanda ya ce raya ababen more rayuwa jigo ne ga samar da ci gaba da dorewar bunkasar tattalin arziki, ya kuma yaba da kwarewar shugabanci da gogewa da ilimi da kuma basirar tsohon firaministan na Kenya.

Mahboub Muaalim ya ce nadin zai taimaka sosai wajen hada karfi da karfe, domin aiwatar da shirin raya ababen more rayuwa na Afrika, yana mai cewa jigo ne cikin ajandar AU ta 2063.

Ya ce a matsayin yankin na wanda ya fi raya ababen more rayuwa, IGAD za ta mara baya ga sabon wakilin wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansa, yana mai bayyana kudurin kungiyar na cimma burin samar da ababen more rayuwa da ci gaban da nahiyar ke bukata. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China