in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar raya gabashin Afrika ta yaba da dagewa Sudan takunkumi da Amurka ta yi
2017-10-11 10:34:13 cri
Sakataren zartaswa na kungiyar raya yankin gabashin Afrika IGAD Mahboub Maalim, ya yaba da dage takunkumin cinikayya da na tattalin arziki da Amurka ta kakabawa Jamhuriyar Sudan gomman shekaru da suka gabata.

Wata Sanarwa da kungiyar ta fitar, ta ce takunkumin da Amurka ta sanyawa Sudan ya haifar da illa sosai ga tsarin tattalin arziki da siyasa da huldar diflomasiyya na kasar.

A madadinsa da kuma kungiyar IGAD, Amb Mahboub ya taya Gwamnati da al'ummar Sudan murna, bisa irin juriyarsu da fata na gari da dabarun diflomasiyya da suka nuna, duk da dimbin kalubalen da suka fuskanta lokaci mai tsawo na tukunkumin.

Amb Mahboub, ya kuma yabawa Amurka da wannan mataki da ta dauka da zai yi kyakkyawan tasiri ba kadai ga tattalin arzikin Jamhuriyar Sudan ba, har ma da kasashe makwabta da na kungiyar IGAD baki daya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China