in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen gabashin Afirka sun hadu domin fidda tsarin samar da Ilimi ga 'yan gudun hijira
2018-07-20 10:20:32 cri
Kasashen gabashin Afirka sun yi wani zama na musamman a Addis Ababa, domin tabbatar da wani tsari da zai baiwa dubun dubatar 'yan gudun hijirar yankin dama ta samun ilimi.

Wata sanarwa da kasashe mambobin kungiyar raya yankin na gabashin Afirka ko IGAD a takaice suka fitar ta bayyana cewa, masu ruwa da tsaki ciki hadda kwararru a fannin raya ilimi sun gana, a wani mataki na amincewa da yarjejeniya, da tsarin gudanarwar Djibouti da aka cimma a watan Disambar shekarar bara.

Sanarwar ta ce, ana fatan masana a fannin raya ilimi na yankin za su fitar da wani tsari na hadin gwiwa, wanda kasashen yankin za su yi amfani da shi wajen aiwatar da waccan yarjejeniya ta Djibouti.

Da yake tsokaci game da hakan, ministan ma'aikatar ilimi na kasar Habasha Mohamed Ahmedin, ya ce ilmantar da 'yan gudun hijira, da wadanda suka rasa matsugunnan su, da ma mazauna yankunan dake karbar su, zai taimaka matuka wajen wanzar da zaman lafiya da daidaito a yankin.

Wani rahoto na MDD ya bayyana kasar Uganda, a matsayin ta daya a kasashen yankin dake karbar 'yan gudun hijira mafiya yawa, inda a yanzu take da sama da 'yan gudun hijirar miliyan 1.4, mafi yawan su daga kasashen Sudan ta kudu. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China