in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Putin na sa ran za a ci gaba da tattaunawa kan batun atisayen dakarun Nato
2018-11-12 10:22:15 cri
Shugaban Rasha Vladimir Putin, ya ce kasarsa na mayar da martani cikin lumana, game da babban atisayen sojin kungiyar tsaro ta NATO na baya-bayan nan, kuma tana fatan ci gaba da tattauna batun.

Da yake ganawa da wani gidan talabijin na kasar Russia Today, Vladimir Putin, ya ce zancen gaskiya shi ne, suna kokarin kauracewa gudanar da atisayen soji a kusa da iyakar kasashe mambobin NATO, amma kuma, za su mayar da martani kan batun cikin lumana.

Kungiyar NATO, ta gudanar da babban atisayen sojinta na bana a Norway da kuma tekunan da suka kewaye ta, daga ranar 25 ga watan Oktoba zuwa 7 ga watan nan, atisaye mafi girma da ta yi tun bayan karshen yakin cacar baka.

Shugaba Putin ya ce yana fatan tattaunawa, wadda ita ake bukata a ko da yaushe, za ta yi kyakkywan tasiri kan yanayin.

Shugban ya kuma ce zai mara baya ga shawarar kafa rundunar kawance ta kasashen Turai don ta maye gurbin Kungiyar tsaro ta NATO. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China