in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNHCR ta mayar da 'yan gudun hijira 44 daga Libya zuwa Italiya
2018-11-12 10:07:51 cri
Babbar hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD (UNHCR) ta bayyana cewa, a wannan makon ta mayar da 'yan gudun hijira 44 zuwa Italiya daga kasar Libya.

Wata sanarwa ta hukumar ta fitar a jiya Lahadi, ta bayyana cewa, 'yan gudun hijira 44 daga kasashen Syria,da Sudan da Palasdinu sun isa kasar Italiya lami lafiya, a wani bangare na shirin hukumar game da sake tsugunar da 'yan gudun hijira.

Shirin raya arewacin Afirka wanda hukumar tarayyar turai tare da gamayyar kasashen turai 14 gami da kasar Italiya wadda ke jagorantar shirin ne suke aiwatar da shirin sake tsugunar da 'yan gudun hijirar kasar ta Libya .

Kasar Libya dai ta kasance zangon da bakin haure ke amfani da ita wajen shiga kasashen turai ta hanyar tsallaka tekun Bahar Rum, sakamakon matsalar tsaro da kasar ke fama da ita, biyo bayan boren shekarar 2011 wanda ya kai ga kifar da tsohon shugaban kasar marigayi Muammar Gaddafi.

Dubban bakin haure ne dai ke makare a wuraren tsugunarsu wadanda da aka ceto a teku ko hukumomin tsaron kasar suka damke. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China