in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
CERF ya samar da dala miliyan 15 don taimakawa mutanen da suka rasa matsugunansu a Habasha
2018-07-13 12:27:28 cri
Asusun tallafin gaggawa na MDD(CERF) ya samar da dala miliyan 15 don agazawa wadanda fadan kabilanci ya raba da muhallansu a kasar Habasha。

Babban sakataren MDD Antonio Guterres wanda ya sanar da hakan jiya Alhamis, ya ce, sabbin matakan samar da hadin kai da sasantawa da gwamnatin firaministan Habasha Abiy Ahmed ta dauka, sun taimaka matuka, kana fadan kabilanci ya haifar wa sabuwar gwamnatin kalubale.

Guterres ya ce, kimanin mutane miliyan 1 ne fadan ya raba da matsugunansu, wadanda ke bukatar taimakon gaggawa. Sai dai ana fuskantar wahalar shiga wasu wuraren saboda shigowar damina. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China