Da yake karin haske cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai, kakakin fadar shugaban kasar ya ce shugaba Ali Bango yana kara samun lafiya matuka.
A ranar 24 ga watan Oktoba ne dai shugaban ya fara jin kasala da hajijiya a lokacin da yake zaune a wani Otel a birnin Riyadh na kasar Saudiya. Bayan da likitansa ya duba shi ne kuma aka garzaya da shi asibitin sarki Faysal dake birnin na Riyadh domin a kara duba lafiyarsa. (Ibrahim)