in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gabon zata kafa wani tsarin rigakafin kamuwa da cutar Ebola
2018-05-18 10:50:30 cri
Ma'aikatar lafiyar kasar Gabon tare da hadin gwiwar hukumar lafiya ta duniya (WHO) zasu kafa wani tsarin bada kariyar dakile yaduwar cutar Ebola bayan da aka samu bullar kwayar cutar a jamhuriyar demokaradiyyar Kongo (DRC).

Hukumomin kasar ta Gabon sun bayyana cewa, ya zama tilas su karfafa ayyukan jami'an kiwon lafiyar kasar da masana yaduwar kwayoyin cutaka don tsananta bincike a kan iyakokin kasar da filayen jiragen sama.

A cewar hukumar ta WHO, kasashen jamhuriyar Kongo, da jamhuriyar tsakiyar Afrika CAR, da kuma Gabon, suna daga cikin jerin kasashen dake cikin hadarin kamuwa da cutar. Sai dai kawo yanzu ba'a samu rahoton bullar cutar ta Ebola ba a kasar Gabon.

Domin daukar matakan kariya, hukumomin kasar Gabon sun yanke shawarar daukar matakai da suka hada da dakatar da zirga zirgar jiragen sama dana ruwa tsakaninta da kasashen da aka samu bullar cutar, sannan zata dakatar da bada takardun izinin shiga kasar ta Gabon ga fasinjoji da suka fito daga kasashen da aka samu rahoton bazuwar cutar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China