Da yake karanta wata sanarwar shugaba, babban sakatare a fadar shugaban kasa Jean Yves Teal, ya ce, shugaba Ali Bongo Ondimba na Gabon ya umarci Issoze-Ngondet da ya kafa sabuwar gwamnati.
A ranar 1 ga watan Mayun wannan shekara ce dai Isso-Ngondet ya yi murabus, sakamakon wata shawara da kotun kundin tsarin mulkin kasar ta yanke na rushe majalisar dokokin kasar, saboda karewar wa'adinta na shekaru biyu, don a kuma bukatar ganin an shirya zabe a kan lokaci.
Kotun dai ta rushe gwamnatin ne saboda ta gaza shirya zabukan majalisar dokoki. (Ibrahim Yaya)