in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Iran ta yi watsi da tasirin da takunkuman Amurka kan fitar da mai ka iya yi mata
2018-10-15 10:37:13 cri
Shugaban Iran Hassan Rouhani, ya ce takunkuman Amurka da za su fara aiki a watan Nuwamba kan man da kasar ke fitarwa, ba za su yi tasiri kan tattalin arziki da rayuwar al'ummar kasar ba.

Shugaba Rouhani ya bayyana haka ne jiya Lahadi a Jami'ar Tehran.

Gidan talabijin na Press ya ruwaito shugaban na cewa, takunkuman da za su fara aiki ranar 4 ga watan Nuwamba ba za su yi tasiri kan harkokin kasar ba, sai dai ya ce manufar matsin lambar ta Amurka ita ce neman sauya gwamnatin Iran.

A ranar 8 ga watan Mayun da ya gabata ne Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da janyewar kasarsa daga yarjejeniyar nukiliyar Iran, inda kuma ya lashi takobin sake kakabawa kasar takunkumai mafi tsauri da aka taba sanya mata.

Zagaye na farko na takunkuman da Amurka ta kakabawa Iran a ranar 7 ga watan Agusta, ya haramtawa Iran din sayen takardar kudin dala da karafa, wanda wani bangare ne na yunkurin yanke kasar daga tsarin hada-hadar kudi ta duniya.

Zagaye na biyu na takunkuma kuwa, sun shafi man fetur da isakar gas da Iran din ke fitarwa, wadanda za su fara aiki a ranar 4 ga watan Nuwamba mai zuwa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China