in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Najeriya ya amince da sabon tsarin albashi
2018-11-07 09:10:47 cri
Shugaban tarayyar Najeriya Muhammadu Buhari, ya amince da bukatar kungiyoyin kwadagon kasar, na neman karin mafi karancin albashi, bayan da 'yan kwadago suka yi barazanar shiga yajin aiki. Amincewar shugaban kasar dai ta kawar da fargabar da aka yi, ta shigar ma'aikata yajin aikin gama gari a dukkanin fadin kasar.

Da yake tabbatar da hakan a jiya Talata a birnin Abuja, fadar mulkin kasar, Shugaba Buhari, ya alkawarta tura wani kudurin doka zuwa majalissar dokokin kasar, wanda zai tabbatar da aiwatar da karin albashin, bayan da ya karbi rahoton kwamiti mai bangarori uku na masu ruwa da tsaki, wanda ya nazarci batun karin albashin.

Shugaban ya ce gwamnatinsa na mai da hankali matuka ga batun karin albashin, yana mai kira ga ma'aikata 'yan kwadago, da kada su bari a yi amfani da su wajen cimma burin siyasa.

Gabanin hakan dai kungiyoyin 'yan kwadago a Najeriyar sun shirya shiga yajin aiki na sai baba ta gani tun daga jiya Talata, suna masu zargin gwamnatin kasar da gaza cika alkawuran da ta yi a baya, na karawa ma'aikatan kasar albashi kamar yadda doka ta tanada. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China