in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Adadin wadanda suka mutu sanadiyyar rikici a arewacin Nijeriya ya kai 78
2018-10-24 09:29:49 cri
Kawo yanzu, mutane 78 ne aka tabbatar sun mutu sanadiyyar rikicin da ya barke makon da ya gabata, a jihar Kaduna dake arewacin Nijeriya.

An samu karuwar adadin ne bayan jami'ai a jihar sun tabbatar da mutuwar karin mutane 23 da jikkatar wasu 17, sakamakon bazuwar da rikicin ya yi zuwa birnin jihar a ranar Lahadin da ta gabata.

Da yake ganawa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua ta wayar tarho, shugaban hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Ben Kure, ya ce gwamnati na kokarin shawo kan rikicin.

Rikicin na baya-bayan nan a Kaduna, wadda ta kasance daya daga cikin jihohin da ta fuskanci yawan hare-hare a kasar, ya fara ne a ranar Alhamis da ta gabata a Kasuwar Magani, wani kauye dake da nisan kilomita 31 daga birnin jihar.

Rahotanni sun ce rikicin ya barke ne sanadiyyar sabanin da aka samu kan wurin da 'yan kasuwa za su rika sauke kayansu na sayarwa a ranar Alhamis da ake cin kasuwar kauyen. Da farko, mutane 50 ne aka tabbatar sun mutu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China