in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijeriya ta tabbatar da mutane 79 ne za su tsaya takarar shugabancin kasar a zaben 2019
2018-10-27 15:12:20 cri
Hukumar zabe mai zaman kanta ta Nijeria wato INEC, ta tabbatar da cewa 'yan takara 79, ciki har da shugaban kasar mai ci Muhammadu Buhari ne za su tsaya takarar shugabancin kasar a zaben badi dake tafe.

Shugaban hukumar INEC Mahmood Yakubu, ya ce jimilar mutane 6,352 ne za su tsaya takarar mambobin majalisun dokokin kasar biyu. Sannan jam'iyyun siyasa 91 za su fafata a babban zaben na 2019.

Mahmood Yakubu ya bayyanawa manema labarai a jiya cewa, ana ci gaba da shiryawa zaben yadda ya kamata, bisa tanadin jadawalin zaben da hukumar ta riga ta fitar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China