in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Amurka sun hallaka mayakan al-Shabab 4 a kudancin Somaliya
2018-11-05 11:38:03 cri
Hukumar gudanarwar sojojin Amurka ta sanar da cewa, a ranar Asabar sojojinta sun kaddamar da hare-hare ta sama a kusa da yankin Araara, dake kudancin kasar Somalia, inda suka kashe mayakan al-Shabab 4.

Rundunar tsaron hadin gwiwa ta Amurka da Afrika wato (AFRICOM), ta ce hare-haren ta sama an kaddamar da su ne bisa hadin gwiwa da jami'an tsaron gwamnatin kasar Somaliya.

Rundunar sojojin ta Amurka ta ce sun kaddamar da hare-haren ta sama ne bayan da suka gano wata makarkashiya da mayakan ke shiryawa na yunkurin kaddamar da hari kan jami'an tsaron hadin gwiwar a lokacin da suke aikin sintiri.

Sojojin Amurka, tare da hadin gwiwar dakarun tsaron gwamnatin Somaliya da kuma dakarun wanzar da zaman lafiya na kungiyar tarayyar Afrika, suna gudanar da aikin tsaro na hadin gwiwa domin murkushe mayakan al-Shabab a Somaliya, da nufin fatattakar kungiyar mai biyayya ga kungiyar al-Qaida wajen hana ta samun sukunin daukar karin mayaka aiki, da ba su horo, don su samu damar kaddamar da hare-haren ta'adanci a ciki da wajen kasar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China