in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da suka mutu a harin tagwayen boma bomai a garin Baidoa na Somaliya ya kai 22
2018-10-14 19:57:25 cri
Hukumomi a Somaliya sun sanar a yau Lahadi cewa yawan mutanen da suka mutu a sanadiyyar harin tagwayen boma bomai a ranar Asabar a garin Baidoa na kudancin kasar Somaliya ya karu zuwa 22 yayin da wadanda suka samu raunuka ya karu zuwa mutane 30.

Gwamnan lardin Bay, Ali Wardhere Doyow, ya fadawa manema labarai cewa al'ummar yankin suna bayar da gudumowar jini domin ceto rayukan wadanda suka jikkata a harin tagwayen boma boman na garin Baidoa, ya kara da cewa, wadanda suka samu munanan raunuka za'a garzaya da su zuwa birnin Mogadishu a yau Lahadi domin yin musu magani. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China